Kwankwaso ya tafi ƙasashen waje bayan  nuna ɗumbin goyon baya daga al’ummar Kano

Rabiu Kwankwaso Kano 750x430

Jagoran tafiyar Kwankwasiyya, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya bar Najeriya bayan halartar muhimman abubuwa biyu a ranar Alhamis.

Kwankwaso ya bar Kano ne jim kaɗan bayan kai ziyara Kasuwar Singer da ke cikin birnin domin jajanta wa ’yan kasuwa sakamakon gobarar da ta tashi a ranar Talata, wadda ta lalata kadarori na Miliyoyin Naira.

Taron magoya bayan da suka mamaye ayarin motocin tsohon gwamnan Jihar Kano kuma ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NNPP a zaɓen gama-gari na 2023, mutane da dama sun kallace shi a matsayin nuna ƙarfin siyasa a titunan birnin.

Duk da cewa ana ta rade-radin cewa tafiyar tasa zuwa ƙasashen waje ta shafi neman kulawar lafiya, kamar yadda kakakin Kwankwasiyya, Kyaftin Mansur Kurugu, ya tabbatar da tafiyar amma ya ƙaryata zargin cewa tafiyar ta shafi rashin lafiya.

Kurugu ya bayyana cewa jagoran Kwankwasiyya ba ya fuskantar wata matsalar lafiya ko kaɗan, yana mai cewa tafiyar ta kasance ta sirri.

Ya ƙara da cewa bai san ƙasar da Kwankwaso ya nufa ba, tunda tafiyar ba ta da alaƙa da harkokin jama’a.

Karin karatu: NBA za ta kai ƙarar Kwankwaso ga ’yan sanda kan zargin tsoma baki a zaɓen shekarar 2019

Ya danganta jita-jitar da ke yawo da yunƙurin wasu na karkatar da hankali daga gagarumin goyon baya da kuma muhimmancin siyasar Injiniya Rabiu Musa Kwankwaso a wannan lokaci, musamman ganin irin taron magoya bayan da suka fito daga ƙaramar hukumar Dawakin Kudu da kuma yadda aka tarbe shi a Kasuwar Singer.

Wannan yanayi na faruwa ne a daidai lokacin da ake samun saɓanin siyasa tsakanin gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, da ubangidan siyasar sa, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, biyo bayan sauya sheƙar gwamnan zuwa jam’iyyar APC.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here