Majalisar dokokin jihar Rivers ta zargi gwamna Siminalayi Fubara da mataimakiyarsa Ngozi Odu da rashin da’a.
A cewar sanarwar da aka aike wa kakakin majalisar dokokin jihar Ribas Martin Amaewhule, ‘yan majalisar sun ce matakin ya dace da kundin tsarin mulkin Najeriya.
“A bisa bin sashe na 188 na kundin tsarin mulkin tarayyar Najeriya na shekarar 1999 (kamar yadda aka yi masa kwaskwarima) da sauran wasu manyan dokoki, mu ‘yan majalisar dokokin jihar Ribas da muka rattaba hannu a kai muna mika muku sanarwar rashin da’a da mataimakiyar gwamnan jihar Rivers ta yi wajen gudanar da ayyukan ofishinta,”.
Kamar yadda sanarwar ta fita a ranar Litinin din nan.
Karin bayani na nan tafe…….