Kwamishinan Sufuri na Jihar Kano, Ibrahim Namadi, ya tsaya wa wani da ake zargi da laifin Dillancin miyagun ƙwayoyi, Suleiman Danwawu.
Kwamishinan ya shige gaba ne tare da karɓar belin wanda ake zargi da laifin sha da dillancin miyagun ƙwayoyi ne bayan da alƙalin kotun mai shari’a MS Shu’aibu, ya sanya wasu sharuddan beli mai tsauri.
Kotun ta bayar da belin wanda ake zargin ne a ranar 16 ga watan Yuli, jaridar DAILY NIGERIAN ta ruwaito cewa, alkalin kotun ya umarci wadanda ake tuhuma da su gabatar da kwamishina mai ci kuma mamba a majalisar zartarwa ta jihar Kano a matsayin wanda zai tsaya masa tare da biyan naira miliyan biyar.
Sai dai abin da ya zama babban aiki na samar da dan majalisar Gwamna Abba Yusuf ya tsaya a matsayin wanda zai tsaya wa wanda ake zargi da laifin dillalan miyagun kwayoyi, Malam Namadi, ya nemi sauƙaƙa wa wanda ake zargin inda ya tsaya masa tare da rubuta wa kotu takarda, ya tsaya a matsayin wanda zai karɓe shi beli.
A wata wasika mai dauke da kwanan watan 18 ga watan Yulin shekarar nan da muke ciki ta 2025 kuma aka aika zuwa ga mataimakin babban magatakarda na babbar kotun tarayya da ke Kano, Kwamishina Namadi ya nemi ya tsaya wa Danwawu.
Wasikar, wadda DAILY NIGERIAN ta samu ta bayyana cewa: “Ina matukar son in nemi tsaya wa wanda ake kara a wannan shari’a (SULAIMAN AMINU) wanda wannan babbar kotu ta bayar da belinsa a kan kudi Naira Miliyan Uku (N3,000,000.00) da mutum daya tsayayyiya a makamancinsa (N5,000), wanda za a sanya shi a cikin Asusu. “Na yi alkawarin mutunta sharuddan belin wanda ake tuhuma kuma na yi alkawarin gabatar da shi a gaban Kotu a duk ranakun da aka dage zaman har zuwa lokacin da za a yanke hukuncin karshe, ina fatan za a yi la’akari da bukatata.”
Da aka tuntube shi don jin ta bakinsa kan lamarin, Malam Namadi ya ce, ya na cikin wani taro, inda ya yi alkawarin kira idan ya kammala.
Har zuwa lokacin gabatar da wannan rahoto bai kira ba.
Idan dai za a iya tunawa, a ranar 21 ga watan Mayu, hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta NDLEA, ta gabatar da tuhume-tuhume guda takwas da suka shafi safarar miyagun kwayoyi a babbar kotun tarayya dake Kano a kan Danwawu.
Bayan gurfana a gaban kotu a ranar 28 ga watan Mayu, an dage sauraron karar zuwa ranar 16 ga watan Yuni domin sauraren neman belin. Daga baya aka tasa keyar wanda ake tuhuma a gidan yari.
Bisa la’akari da sha’awar jama’a da shari’ar ta haifar, kungiyar lauyoyin Najeriya NBA reshen jihar Kano ta bayyana aniyar ta na sanya ido sosai kan shari’ar da ake yi wa Danwawu.













































