Tinubu ya miƙa ta’aziyyar Imam Idris Abdulaziz Dutsen Tanshi

IMG 20250404 WA0002 710x430

Shugaban kasa Bola Tinubu, ya bayyana alhininsa game da rasuwar babban malamin addinin musuluncin nan mazaunin Bauchi, Dr Idris Abdulaziz Tanshi, yana da shekaru 68 a safiyar yau Juma’a.

Tinubu ya ce malamin ya bayar da gudunmawa wajen gyare-gyaren miliyoyin matasa da sauran musulmi masu imani a kan tsarin addinin Musulunci.

Bayo Onanuga, mai magana da yawunsa, ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa.

Shugaban ya yaba da kokarin malamin wajen dakile yaduwar munanan ayyukan ta’addanci, musamman a farkon rikicin Boko Haram.

Ya ce musulmi mai imani zai yi matukar kewar muryar sa, yana mai kira da a daidaita dabi’u da halayya.

Yayin da yake addu’ar Allah ya jikan Tanshi, Tinubu ya bukaci iyalansa da mabiyansa da su yi koyi a cikin kyakkyawan aikinsa. (NAN)

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here