Tawagar Gwamnan Abia ba ta gamu da harin ‘yan bindiga ba – Sakataren yaɗa labarai

Osun governor Ademola Adeleke 750x430

Sakataren yaɗa labaran Gwamna Alex Otti na jihar Abia, Ukoha Njoku, ya bayyana gaskiyar abin da ya faru game da rahoton da ke yawo cewa an kai wa tawagar gwamnan hari.

A wata sanarwa da ya fitar a ranar Talata, Njoku ya ce wani rukuni na ma’aikata uku daga ofishin gwamnan da ke Umuahia, waɗanda ke aiki a filin jirgin Sama Mbakwe na Owerri, ne ‘yan bindiga suka kai wa hari a hanyar da ke tsakanin Umuowa da mahaɗar Ihitte yayin da suke kan hanyarsu zuwa filin jirgin.

Ya tabbatar da cewa tawagar gwamnan ba ta cikin abin da ya faru, inda ya jaddada cewa babu wanda ya rasa ransa a lamarin.

A cewar sanarwar, harin ya faru ne da safiyar ranar Talata 2 ga Disamba, lokacin da ma’aikatan uku daga ofishin gwamnan ke kan aiki a filin jirgin Sam Mbakwe na jihar Imo.

Sanarwar ta bayyana cewa lamarin ya faru ne tsakanin Umuowa da mahaɗar Ihite, kusa da hanyar shiga filin jirgin Sam Mbakwe a jihar Imo.

Sanarwar ta tabbatar da cewa tawagar Gwamna Otti ba ta cikin harin, kuma babu asarar rai da ta auku a wannan abin bakin ciki.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here