Tawagar ƙwararru ta NAHCON ta tashi zuwa Makkah domin kaddamar da aikin Hajji

NAHCON 1

Hukumar kula da aikin hajji ta ƙasa NAHCON ta fara gudanar da aikin Hajjin bana na 2025 a hukumance, ta hanyar fara tura tawagarta da ta tashi zuwa kasar Saudiyya.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da babban jami’in yada labarai na hukumar NAHCON, Shafii Mohammed ya fitar a Abuja ranar Litinin.

Mohammed ya bayyana cewa tawagar da ta kunshi manyan jami’an gudanarwa da kuma manyan jami’an kungiyar likitocin ta kasa sun bar Abuja ne a ranar Litinin bayan wani bikin bankwana da aka yi.

Daraktan gudanarwa da ma’aikata, Alhaji Babagana Bukar, ya yabawa yadda tawagar ta gudanar da aikin Hajjin da ya gabata tare da jaddada amincewarsa ga ‘yan kungiyar.

Ya kuma yi kira ga Shugaban Hukumar NAHCON, Farfesa Abdullahi Saleh, da hukumar gudanarwar su da su ci gaba da ba kungiyar goyon baya domin ganin an samu nasarar aikin.

Karin karatu: Ɗalibai 420,415 cikin su miliyan 1.95 ne kaɗai da suka rubuta UTME suka samu maki sama da 200 – JAMB

A nasa jawabin, shugaban NAHCON Farfesa Abdullahi Sale Usman ya bukaci kungiyar da ta tunkari wannan aiki da himma da kwazo, tare da jaddada tsaftar aikin da ke gabanta.

Ya ba su tabbacin goyon bayan hukumar tare da tunatar da su da su ji tsoron Allah yayin da suke gudanar da ayyukansu.

A nasa bangaren, Farfesa Abubakar Yagawal, Kwamishinan Tsare-tsare, Bincike, Kididdiga, yada Labarai da Ayyukan dakin bincike (PRSILS), ya bayyana rawar da tawagar ta taka a matsayin yar tsakiya da dabarun samun nasarar aikin.

Dokta Mustapha Sani, Sakataren Hukumar, ya tabbatar wa tawagar cewa tuni shugaban ya amince da kunshin jin dadin jama’a, inda ya jaddada kudirin NAHCON na tallafawa ma’aikata a duk lokacin aikin Hajji.

Malam Alidu Shutti daraktan sa ido da bin ka’ida kuma mataimakin kodineta a garin Makkah wanda ya yi magana a madadin tawagar ya nuna jin dadinsa da amanar da aka basu.

Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya NAN ya ruwaito cewa tawagar farkon ce ke da alhakin kafa harsashin gudanar da aikin Hajji baki daya da suka hada da shirye-shiryen masauki, ka’idojin karbar filin jirgin sama da kuma hada kai da hukumomin Hajjin Saudiyya.

Yunkurin tawagar zai share fagen isowa tare da jin dadin alhazan Najeriya da ma’aikatan lafiya da jami’an jihohi. (NAN)

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here