Taron ƙungiyar Editoci: Tinubu, Gwamnonin jihohi, Ministoci da shugabannin kafafen yaɗa labarai za su halarci bude shi

NGE NGE

An kammala duk shirye-shirye don gudanar da taron ƙungiyar Editocin Najeriya karo na 21 (ANEC), wanda za a fara gudanar a birnin tarayya Abuja daga ranar Laraba, 12 ga Nuwamba, 2025.

Za a gudanar da taron na tsawon kwanaki biyu, inda shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu zai buɗe shi a cibiyar taro ta fadar gwamnati da ke Aso Villa, tare da halartar gwamnonin jihohi, shugabannin kafafen yada labarai, jakadu, masana, da sauran manyan baki.

A cikin wata sanarwa da shugaban ƙungiyar Editoci ta Najeriya, Eze Anaba, da sakatare janar Onuoha Ukeh suka fitar, an bayyana cewa akalla editoci dari biyar daga sassa daban-daban na ƙasar za su halarci taron.

Ƙungiyar ta ce sarkin Sakkwato, Mai Alfarma Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar, da kuma yariman asalin yankin Delta, Nduka Obaigbena, wanda ke shugabantar kamfanin jaridar This Day da gidan talabijin Arise News, za su kasance shugabannin taron, yayin da gwamnan jihar Imo, Sanata Hope Uzodimma, zai gabatar da jawabi na musamman.

Karanta: Gwamnan Kano da Ganduje sun hadu a karon farko tun bayan miƙa mulki sama da shekaru biyu

Jaridar Solacebase ta rawaito cewa shugabannin kafafen yada labarai kamar tsohon gwamnan jihar Ogun, Cif Segun Osoba; Cif Onyema Ugochukwu; Femi Adesina; Mallam Garba Shehu; Dakta Orji Ogbonnaya Orji, sakataren gudanarwa na hukumar NEITI; da Ukpe Anietie, mataimakin shugaban ma’aikatan majalisar Dattawa, na daga cikin mahalarta taron.

Taron mai taken “Gudanar da dimokuradiyya da haɗin kan ƙasa: Rawar da Editoci ke takawa” zai tattauna kan yadda kafafen yada labarai za su tallafa wa ci gaban dimokuradiyya da haɗin kan ƙasa, tare da duba kalubale da hanyoyin da za su inganta wannan aiki kafin babban zaɓen shekarar 2027.

A ranar farko ta taron, lauya kuma babban mai shari’a, Farfesa Awa Kalu (SAN), zai yi bayani kan “Rigimar zaɓe da gaskiyar shari’a: Tsakanin doka da siyasa.” Daga nan sai Farfesa Sheriff Ghali Ibrahim daga jami’ar Abuja ya gabatar da muhawara kan “Yanayin ƙasa: Bukatar gyaran tattalin arziki da siyasa.”

A rana ta biyu, a cibiyar taro ta rundunar sojin sama, tsohon shugaban tsaron ƙasa, Janar Lucky Irabor, zai tattauna kan “Kafafen yada labarai, ta’addanci da tsaron ƙasa,” yayin da Farfesa Abiodun Adeniyi daga jami’ar Baze zai yi bayani kan “Sauyin aikin jarida: Kalubalen bayanan bayyanar fasahar AI da rashin amincewa.”

Ƙungiyar ta bayyana cewa za a gudanar da zama na musamman a rana ta ƙarshe, inda editoci za su tattauna kai tsaye da jami’an gwamnati da shugabannin kamfanoni.

Haka kuma, kungiyoyin da ke haɗa kai da taron sun haɗa da kamfanin jiragen sama Air Peace, kamfanin man fetur na ƙasa NNPCL, da ma’aikatar bayanai da tsare-tsaren wayar da kai ta tarayya.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here