Shugaban Ƙaramar Hukuma a Katsina ya rasu

IMG 20250610 WA0014

Sabon zababben shugaban karamar hukumar Bakori ta jihar Katsina, Aminu Dan Hamidu, ya rasu bayan watanni biyu da hawansa mulki.

Hamidu, wanda ya fara aiki a hukumance a watan Afrilun bana bayan zaben kananan hukumomi na watan Fabrairu, ya rasu a jiya Litinin.

Yayin da ba a bayyana ainihin musabbabin mutuwarsa a hukumance ba, rahotonni da ba a tabbatar ba sun nuna cewa ya dade yana fama da rashin lafiya.

IMG 20250610 WA0013

Marigayi Marigayi Aminu Dan Hamidu

Babban Sakataren Yada Labarai na Gwamna Dikko Umaru Radda, Kaula Mohammed, ya tabbatar da faruwar lamarin a cikin wata sanarwa da ya fitar a hukumance.

Gwamna Radda ya bayyana matukar kaduwarsa game da rasuwar Hamidu, inda ya kwatanta shi a matsayin “mutumin kirki mai nagarta kuma, gogaggen ma’aikacin gwamnati, kuma dan siyasa mai kishin kasa wanda ya sadaukar da rayuwarsa wajen yi wa jama’a hidima cikin gaskiya, tawali’u da kuma sadaukarwa ta musamman.”

Duk da takaitaccen lokacin da ya yi, a kan mulki, Gwamnan ya ce, Hamidu ya gudanar da mulki na gaskiya da kuma sadaukar da kai ga ci gaban al’umma.

Ya lura cewa shekarun Hamidu yana aiki a matakai daban-daban na gwamnati, an bayyana su ta hanyar aiki tukuru da kuma zurfin fahimtar da hidima ga jama’a.

A madadin gwamnati da al’ummar jihar, Gwamna Radda ya mika sakon ta’aziyya ga iyalan Hamidu da al’ummar Bakori har ma da ‘ya’yan jam’iyyar APC a fadin jihar.

Ya kuma yi alkawarin cewa gwamnati za ta ci gaba da tunawa da marigayin bisa halin kunya da jajircewa da kuma irin kaunar da ya yi wa al’ummarsa.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here