Shirin horar da ƙwararrun ma’aikatan lafiya a ƙasa kaso 2.0 zai sauya tsarin bayar da lafiya a Kano – Mahukunta

WhatsApp Image 2026 01 16 at 22.18.31 750x430 (1)

Ma’aikatar lafiya ta jihar Kano tare da haɗin gwiwar ma’aikatar lafiya da walwalar jama’a ta tarayya sun ƙaddamar da wani shirin horaswa na ƙwararrun lafiya da aka tsara domin sauya fasalin tsarin bayar da hidimomin lafiya a faɗin jihar Kano.

Shugaban ƙaramar hukumar Gaya kuma wakilin ƙungiyar shugabannin ƙananan hukumomin Nijeriya kan harkokin lafiya, Muhammad Tajo Sani Gaya, ya bayyana ƙaddamar da shirin, inda ya nuna cewa an gudanar da tsauraran matakai na tantancewa kafin zaɓen mahalarta.

Bayan kammala wannan tsari mai tsawo, an zaɓi ƙwararrun ma’aikatan lafiya 132 daga cikin sama da masu neman shiga shirin 100,000, abin da ya nuna muhimmanci da girman shirin ga ɓangaren lafiya a jihar Kano.

Jaridar Solacebase ta rawaito cewa an tsara shirin ne domin inganta matakan lafiya ta hanyar bai wa ƙwararrun ma’aikata kulawar ayyukan lafiya a matakin ƙananan hukumomi, bisa daidaito da ƙa’idojin ƙasa da na duniya.

Tsarin zaɓen ya ɗauki kwanaki biyar, inda aka gudanar da tantance takardu, hirarraki da gwaje-gwaje, ƙarƙashin kulawar kwararrun masana lafiya ciki har da likitoci huɗu masu fannoni daban-daban da kuma wakilin hukumar lafiya ta duniya.

An tsara shirin ne ta yadda kowace ƙaramar hukuma 44 a jihar Kano za ta samu wakilai uku, domin tabbatar da adalci da rarraba dama yadda ya dace a faɗin jihar, tare da mayar da hankali musamman ga yankunan karkara da wuraren da ke da ƙarancin hidimomin lafiya.

Ana sa ran wannan shiri zai taka muhimmiyar rawa wajen rage gibin hidimomin lafiya, domin ƙwararrun da aka zaɓa za su samu cikakken horo kafin fara aiki, abin da zai ƙarfafa basirarsu da kuma dacewa da tsarin aikin lafiya da ake amfani da shi a jihar Kano.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here