Alkalin wata babbar kotun tarayya da ke Abuja, Mai shari’a Obiora Egwuatu da aka nada don sauraron karar da Sanata mai wakiltar Kogi ta tsakiya, Natasha Akpoti-Uduaghan ta shigar ya yi watsi da karar a ranar talata tare da janyewar.
Alkalin kotun ya yanke hukuncin ne bisa bukatar da shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio, ya rubuta domin kalubalantar rashin amincewarsa kan lamarin.
Duk da cewa an sanya karar ne a farko don saurare, amma lokacin da magatakardar kotun, Mai shari’a Egwuatu, ya kira karar sai ya yanke hukuncin a wani gajeren hukuncin.
Ya ce za a mayar da daftarin karar zuwa ga babban Alkali domin a mayar da shi ga wani alkali daban.
Idan dai ba a manta ba a ranar 4 ga watan Maris ne mai shari’a Egwuatu ya bayar da umarnin wucin gadi da ya dakatar da kwamitin majalisar dattawa mai kula da da’a, gata da kuma kararrakin jama’a ci gaba da shari’ar ladabtarwa da aka fara a kan Sanata Akpoti-Uduaghan kan zargin da ake yi mata na cewa ta ki bin dokokin majalisar.
Karanta har ila yau: Natasha Akpoti: ‘Yan mazabar Kogi ta tsakiya sun mika koke ga INEC don yi mata kiranye
Ya ci gaba da cewa ya kamata a dakatar da tsarin ladabtarwa, har sai an yanke hukunci kan karar da ‘yar majalisar ta shigar a gabansa.
Bugu da kari, Mai shari’a Egwuatu ya baiwa wadanda ake kara sa’o’i 72 domin su nuna dalilin da ya sa ba za su bayar da umurnin dakatar da su daga gurfanar da mai karar bisa zargin aikata ba daidai ba, ba tare da ba ta damar da ya tanada a kundin tsarin mulki na 1999 ba, kamar yadda aka yi wa kwaskwarima, Dokar Tsare-tsare ta Majalisar Dattawa ta 2023, da Majalisar Wakilai.
Ya ba da izini ga mai ƙara don yin sammaci na asali da kuma duk matakan da suka biyo baya akan duk waɗanda ake tuhuma.
Sai dai duk da umarnin da kotun ta bayar, kwamitin majalisar dattawa ya gudanar da zamansa inda ya caccaki mai karar da dakatar da ita na tsawon watanni shida.
Bayan gabatar da bukatar da wadanda ake kara suka gabatar, Mai shari’a Egwuatu daga baya ya yi gyara ga umarnin wucin gadi da ya bayar na goyon bayan wanda ya shigar da karar, ta hanyar ficewa daga bangaren da ya haramta wa majalisar dattijai yin duk wani aiki da ya dace da karar.
Shugaban majalisar dattawan ta bakin tawagarsa ta lauyoyin da ke karkashin jagorancin Mista Kehinde Ogunwumiju, SAN, sun nemi kotun ta daina yin katsalandan a cikin harkokin majalisar.













































