PDP ta sake ɗage babban taronta na ƙasa

PDP PDP 750x430

Babbar jam’iyyar adawa ta PDP ta sake ɗage babban taronta na ƙasa NEC, wanda yanzu aka mayar ranar 15 ga Mayun 2025.

Jam’iyyar ta bayyana haka ne a wata sanarwa da ta fitar, wadda babban sakatarenta, Sunday Ude-Okoye ya sanya wa hannu.

Karin karatu: Atiku yayi watsi da rahotannin sauya sheka Daga jam’iyyar sa ta PDP 

Tun da fari jam’iyyar ta sanar da babban taron ta ne a ranar 13 ga Maris, sannan aka ɗage saboda wasu zaɓukan cike gurbi da aka yi a wasu jihohi da yankuna.

Tun a shekarar da ta gabata ce dai aka saka ranar babban taron na 98, amma ana ɗagewa, wanda wataƙila hakan bai rasa nasaba da wasu matsaloli da jam’iyyar ke fuskanta.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here