Kwamishinan Sufuri na jihar Kano, Alhaji Ibrahim Namadi, ya janye daga yunƙurinsa na karɓar belin wani da ake zargi da laifin dillalancin miyagun ƙwayoyi Suleiman Danwawu, a wata shari’ar da ake yi a gaban babbar kotun tarayya da ke Kano.
Shari’ar tsakanin gwamnatin Tarayya da Sulaiman Aminu mai lamba (FHC/KN/CR/93/2025), ta shafi zargin aikata laifukan da suka shafi muggan kwayoyi.
A baya SolaceBase ta ruwaito cewa, Kwamishina Namadi ya tsaya a matsayin wanda zai tsaya wa wanda ake tuhuma.
Sai dai Ibrahim Namadi a yau Juma’a a hukumance ya janye kansa daga karɓar belin ta cikin wata wasika da ya miƙa wa mataimakin magatakardar kotun.
Wasikar, wadda SolaceBase ta samu a daren yau Juma’a, ta bayyana hukuncin da ya yanke.

A cikin wasikar, Kwamishinan ya kawo dalilai na ƙashin kansa, tare da buƙatar kare mutuncinsa da kuma kare martabar ofishinsa a matsayinsa na jami’in gwamnati.
Ya bayyana cewa ya yanke shawarar fara zama a matsayin wanda zai tsaya masa ne bisa ga ra’ayinsa, saboda alaka ta iyali da ta dade da kuma kula da jin kai.
Idan dai za a iya tunawa, a ranar 21 ga watan Mayu, hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa, NDLEA, ta gabatar da tuhume-tuhume guda takwas da suka shafi safarar miyagun kwayoyi a babbar kotun tarayya dake Kano kan takardun tafiye-tafiyen Danwawu.
Bayan gurfana a gaban kotu a ranar 28 ga watan Mayu, an dage sauraren karar zuwa ranar 16 ga watan Yuni domin sauraren neman belin.
Daga baya aka tasa keyar wanda ake tuhuma zuwa gidan yari.
Bisa la’akari da irin sha’awar jama’a da shari’ar ta haifar, kungiyar lauyoyi ta Najeriya NBA reshen jihar Kano ta bayyana aniyar ta na sanya ido sosai kan shari’ar da ake yi wa Danwawu.












































