Kafofin sadarwar zamani yanzu sun zama ƙungiyar ta’addanci – Sultan

Sultan of Sokoto

Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammadu Sa’ad Abubakar III, ya bayyana kafafen sada zumunta a matsayin “kungiyar ta’addanci”.

Sarkin ya yi wannan jawabi ne a ranar Talata a taron kwamitin zartarwa na majalisar sarakunan Arewa karo na bakwai a Maiduguri.

Sarkin ya ce bai kamata ‘yan Najeriya su bar labaran karya da kage a shafukan sada zumunta ba, domin suna kara tabarbarewar tsaro.

“Dole ne hukumomin tsaro su yi maganin wannan kungiyar ta’addanci da ake kira social media.”

Karin karatu: Hukumar ba da agajin gaggawa ta majalisar ɗinkin Duniya za ta rufe ayyukanta a Najeriya

Alhaji Sa’ad Abubakar ya ce hare-haren da ake kaiwa Filato da sauran sassan kasar abin damuwa ne kuma yana bukatar kulawa cikin gaggawa.

A cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar Litinin, kungiyar kare hakkin bil’adama ta Amnesty International ta ce adadin wadanda suka mutu a harin da aka kai a Filato ya kai 54.

A cewar kungiyar kare hakkin bil adama, daruruwan mutane ne suka rasa matsugunansu tun bayan faruwar lamarin kuma mazauna yankin na cikin fargabar yiwuwar sake kai wani hari.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here