Gwamnatin mulkin sojin jamhuriyar Nijar ta ayyana harshen Hausa a matsayin sabon harshen kasar a hukumance, duk da Faransanci ya fi shahara.
An sanar da matakin ne a cikin wata sabuwar yarjejeniya da aka fitar a ranar 31 ga Maris kuma aka buga a cikin wata jarida ta musamman ta gwamnati.
A cewar sanarwar, Harshen Hausa ya riga ya zama yaren da aka fi amfani da shi a fadin Nijar, musamman a yankunan Zinder, Maradi, da Tahoua.
Galibin al’ummar kasar mai kimanin mutane miliyan 26 sun fahimta kuma suna jin Hausa, idan aka kwatanta, kusan mutane miliyan uku ne kawai, kimanin kashi 13 kawai ke iya magana da Faransanci.
A yayin bikin, gwamnatin mulkin soja ta samu karin goyon baya, kuma an ba shugaban mulkin soja, Janar Abdourahamane Tiani, izinin ci gaba da rike mukamin na tsawon shekaru biyar.
Tun bayan samun mulki a wani juyin mulki a watan Yulin 2023, wanda ya hambarar da shugaban farar hula na kasar, Mohamed Bazoum, gwamnatin mulkin soji ta yanke hulda da Faransa.
Wadannan matakan sun hada da janye sojojin Faransa daga cikin al’ummar kasar, da katse huldar diflomasiyya, da sauya sunayen hanyoyi da gine-ginen da a baya suna da sunayen Faransanci.
Kasashen Nijar da Mali da Burkina Faso da ke da gwamnatocin soji da kuma wadanda Faransa ta yi wa mulkin mallaka na daukar irin wannan mataki.
















































