JAMB ta musanta batun sanyawa ɗalibai garuruwan da suka zaba

Jamb

Hukumar shirya jarabawar shiga manyan makarantun gaba da sakandire ta JAMB ta gargadi jama’a da su guji yada labaran karya na cewa ta na sauyawa dalibai cibiyoyin jarrabawa a maimakon garuruwan da suka zaba.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da mai magana da yawun hukumar Dr Fabian Benjamin ya raba wa manema labarai a Abuja ranar Asabar.

Benjamin ya bayyana cewa JAMB ta fahimci mahimmancin barin dalibi a yankin da ya zaba kuma tana tabbatar da cewa sun rubuta jarrabawar su a wuraren da suka zaba a cikin cibiyoyin yankin.

A cewarsa, kowane dan dalibi yana da hurumin zabar garin da yake son rubuta jarrabawar, kuma hukumar JAMB ta sanya shi wata cibiya dake cikin garin.

Karin karatu: Za a sake bude filin jirgin saman Enugu bayan gyaran titin jirgin – FAAN

A cewar JAMB Ikirarin da ba shi da tushe balle makama na cewa ana tura dalibai zuwa garuruwa daban-daban da abin da suka zaba, kuskure ne, zalunci ne, da nufin bata sunan Hukumar ne kawai, hakan ba ya faruwa. (NAN)

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here