Sufeto-Janar na Ƴansanda, IGP, Usman Baba, ya amince da kafa tawagar tsare-tsare, sa ido da nazari a kan zabe gabanin babban zabe.
Jami’in hulda da jama’a na rundunar, CSP Olumuyiwa Adejobi ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a jiya Laraba a Abuja.
Ya ce za a baza ƴan tawagar a fadin jihohin tarayyar kasar domin tantancewa da kuma daƙile matsalolin tsaro a lokacin zabe.
Adejobi ya ce tawagar za ta gudanar da aikin tantancewa tare da tantance matsugunan tsaro a gabanin babban zabe.
Ya ce kafa wannan tawaga wani ɓangare ne na yunƙurin IGP na tabbatar da tsaro da amintaccen zaɓe.













































