Gwamnatin jihar Kano ta dauki matakin tura sabbin masu gadin daji 100 domin karfafa kokarin kare gandun daji da kuma yaki da kalubalen sare-saren itatuwa, da canjin yanayi ke haifarwa a fadin jihar.
Kwamishinan muhalli da sauyin yanayi na jihar, Dakta Dahiru Muhammad Hashim, ya bayyana hakan a ranar Litinin yayin raba takardun daukar aiki ga sabbin ma’aikatan.
Ya ce wannan shiri na gwamnati “muƙamin tarihi ne” da zai taimaka wajen dakile lalacewar muhalli.
A cewarsa, matakin ya biyo bayan amincewar gwamna Abba Kabir Yusuf wanda ya sanya kare muhalli a matsayin muhimmin bangare na ajandar gwamnatinsa.
Hashim ya bayyana cewa matsalar rashin isassun ma’aikata na daya daga cikin manyan kalubale wajen kare gandun daji, amma yanzu gwamnati ta dauki sabbin ma’aikatan da za su fara aiki nan da nan.
Kwamishinan ya ce babban aikin masu gadin shi ne kare gandun daji daga sare itatuwa ba bisa ka’ida ba da sauran ayyukan da ke lalata muhalli.
Ya kara da cewa gwamnati za ta horas da su, ta ba su kayan aiki, tare da tabbatar da biyan albashi akan lokaci domin karfafa musu gwiwa.
Haka kuma, an samar da layin waya na musamman a ma’aikatar domin kai rahoton duk wani lamari na sare itatuwa cikin gaggawa.
Ya kuma bayyana cewa sabbin ma’aikatan an zabe su ne daga kananan hukumomin da suke zaune, kuma za a bar su su yi aiki a yankunansu domin kara ingantawa da kuma sa su ji aikin ya shafe su kai tsaye.
Ya ce gwamnati za ta ci gaba da shirya horo na zamani domin kara basira da fasaha wajen kare muhalli.
Daya daga cikin sabbin masu gadin daji, Muhammad Kabir, ya bayyana farin cikinsa tare da godewa gwamna da kwamishina bisa damar da suka ba su.
Ya yi alkawarin gudanar da aikinsa da gaskiya da kuma jajircewa wajen kare muhalli da albarkatun jihar.













































