Gwamnan Bauchi ya kori Kwamishina a cikin ƙaramin sauyin da zai samar a majalisar zartarwa

Bala Mohammed 750x430

Gwamnan Jihar Bauchi, Sanata Bala Mohammed, ya kori Hajiya Zainab Baban-Takko daga kujerar Kwamishinar harkokin Mata da cigaban yara nan take.

Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da mai ba gwamnan shawara na musamman kan harkokin yada labarai, Malam Mukhtar Gidado, ya fitar da safiyar Litinin.

A cewar Gidado, wannan mataki na zuwa ne sakamakon ƙaramin sauyi da gwamnan ya yi a cikin tsarin majalisar zartarwar jihar.

Sanarwar ta ƙara da cewa gwamnan ya gode wa kwamishinar bisa gudunmawar da ta bayar ga jihar a lokacin da take rike da mukamin, tare da yi mata fatan alheri a ayyukan ta na gaba.

Haka kuma, sanarwar ta bayyana cewa wannan sauyin wani ɓangare ne na ƙoƙarin gwamnati wajen inganta tsarin gudanarwar jihar domin tabbatar da cigaba ga al’umma.

NAN

 

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here