Gwamna Zulum da Shehun Borno sun buƙaci gwamnatin tarayya ta gaggauta gyara Alau Dam

Zulum Zulum 750x430

Gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Zulum, da Shehun Borno, Alhaji Abubakar El-Kanemi, sun buƙaci Gwamnatin tarayya da ta gaggauta yin aikin gyaran madatsar ruwa ta Alau.

Gwamnan da Shehun Bornon sun mika bukatar hakan ne a lokacin da Shehun ya kai gaisuwar Sallah ga gwamnan a Fadar Gwamnatin jihar dake Maiduguri, inda suka jaddada muhimmancin aikin domin hana afkuwar makamanciyar ambaliyar da aka samu a baya.

Gwamna Zulum ya nuna damuwarsa kan jinkirin aikin, yana mai cewa akwai buƙatar a ɗauki mataki cikin gaggawa kafin zuwan damina. Inda ya yi gargadin cewa, idan ba a hanzarta ba, jihar na iya fuskantar wata ambaliya mai haɗari kamar ta shekarar 2024.

Gwamnatin Tarayya ta amince da ware Naira biliyan 80 don aikin, wanda aka kaddamar a watan Maris.

Wannan roƙo nasu dai na zuwa bayan da al’ummar garin na Alau da ma mazauna Borno suka fara nuna fargaba ganin damina ta fadi.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here