Fitaccen ɗan kasuwa kuma shugaban dandalin dattawan ƙasa masu kishin ƙasa don zaman lafiya da haɗin kai, Alhaji Bature Abdulaziz, ya rasu a birnin Kano.
Alhaji Bature Abdulaziz ya rasu ne bayan gajeriyar rashin lafiya a gidansa da ke kan titin Hadejia a birnin Kano, a ranar Asabar, lamarin da ya jefa iyalansa da al’ummar da ke kewaye da shi cikin jimami.
Babban ɗansa, Abdulaziz Bature Abdulaziz, ya tabbatar da rasuwar mahaifinsa, inda ya nuna cewa ya rasu yana da shekaru 76 bayan fama da gajeriyar rashin lafiya.
Ya ce, an shirya gudanar da sallar jana’izarsa a gidansa da ke Yankaba da misalin karfe 10.00 na safe, inda ake sa ran taron jama’a daga sassa daban-daban na jihar Kano da ma wajenta.
Karanta: Kano: An yiwa wata Mata da yara shida mummunan kisan gilla
Marigayi Bature Abdulaziz an haife shi a shekarar 1950 a Adakawa da ke ƙaramar hukumar Dala ta jihar Kano, inda ya tashi ya zama fitaccen ɗan kasuwa mai tasiri a harkokin kasuwanci.
Ya kasance sananne a matsayin jagoran al’umma kuma mai faɗin albarkacin baki kan batutuwan ƙasa, lamarin da ya sa ya samu girmamawa da karɓuwa a tsakanin jama’a a Kano da ma fadin Nijeriya.













































