DA ƊUMI-ƊUMI: Buhari Ya Sallami Shugaban Hukumar NAPTIP

Basheer Garba Mohammed Lado
Basheer Garba Mohammed Lado

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya kori Sanata Basheer Mohammed Lado, Darakta Janar na Hukumar Hana Fataucin Mutane ta Kasa (NAPTIP).

Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da babban mai taimakawa shugaban kasa na musamman kan harkokin yada labarai, Garba Shehu ya fitar.

Sanarwar ta ce shugaban ya amince da nadin Dr. Fatima Waziri-Azi a matsayin wanda zai maye gurbin Mohammed.

”Nadin ya biyo bayan shawarwarin da ministar kula da ayyukan jin kai da ci gaban al’umma Hajiya Sadiya Umar Farouq ta yi, ” in ji sanarwar.

Ya ce Ministar ta bayyana “bukatar hukumar ta NAPTIP ta kara kaimi domin cimma muhimman nasara.”

A cewar sanarwar, Hajiya Sadiya ta ce Fatima Waziri-Azi tana da asali mai kyau” da gogewa kuma za ta yi amfani ingantacciyar hanyar da ta dace don ciyar da hukumar gaba.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here