Da Ɗumi-Ɗumi: Farfesa Yakubu ya mika ragamar hukumar INEC ga shugabar riƙon ƙwarya

88f063c1 ac2b 4d65 b749 41c377a484f0

Shugaban hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa (INEC) mai barin gado, Farfesa Mahmood Yakubu, ya mika ragamar shugabancin hukumar ga Misis May Agbamuche-Mbu, wadda za ta rike matsayin shugabarl ta riƙon ƙwarya.

An gudanar da bikin mika ragamar ne a ranar Talata yayin taron da yake gudana tsakanin Farfesa Yakubu da kwamishinonin zaɓe na jihohi (RECs) a cibiyar hukumar da ke Abuja.

Misis Agbamuche-Mbu, wadda ita ce tsohuwar kwamishina mafi dadewa a cikin hukumar, za ta kula da harkokin gudanarwa na INEC har sai an naɗa sabon shugaba.

Farfesa Yakubu ya bayyana cewa ya mika shugabancin hukumar a hukumance ga Misis Agbamuche-Mbu, tare da kira ga sauran kwamishinoni da daraktoci su ci gaba da bayar da goyon baya da haɗin kai kamar yadda suka yi masa.

Wannan sauyi ya zo ne a daidai lokacin da hukumar ke ci gaba da shirye-shiryen gudanar da wasu muhimman ayyukan zaɓe a faɗin ƙasar nan.

Kamfanin dillancin labarai na ƙasa NAN ya ruwaito cewa Misis Agbamuche-Mbu, wadda ƙwararriya ce a fannin mulki da lauyanci, ta kasance a cikin kwamitin gudanarwa na INEC tun bayan nadinta, kuma ana sa ran za ta ci gaba da aiwatar da sauye-sauyen da ake gudanarwa a cikin hukumar.

 

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here