Cikakken jadawali: Mai riƙon muƙamin shugabancin jihar Rivers Ibas ya nada shugabannin ƙananan hukumomi, ya sake kafa hukumar zabe

Ibot Ete Ibas

Mai riƙon shugabancin jihar Rivers Vice Admiral Ibok-Ete Ibas, ya amince da nadin sabbin shugabanni da mambobin hukumar zabe mai zaman kanta ta jihar, da kuma shugabannin ƙananan hukumomi.

A cewar sanarwar, sabon shugaban RSIEC, Dr Micheal Ekpai Odey, zai yi aiki da mambobi shida da kuma farfesoshi hudu.

An bayyana nadin ne a wata sanarwa ta musamman da gwamnatin ta fitar ranar Laraba ta hannun Farfesa Ibibia Worika, sakataren gwamnatin jihar Rivers.

Sanarwar wacce aka aike wa manema labarai ta ce nadin ya fara aiki ne daga ranar Litinin 7 ga Afrilu, 2025.

Idan ba a manta ba a makon da ya gabata ne Ibas ya dakatar da shugabannin ma’aikatu da hukumomin jihar da suka hada da RSIEC, karkashin jagorancin Mai shari’a Adolphus Enebeli (mai ritaya).

Shugabannin kananan hukumomi 23 na jihar Rivers sun hada da:

Mr Okroiyobi Animiete – karamar hukumar Abua/Odual

2. Mr Goodluck M. Ihenacho – karamar hukumar Ahoada ta gabas

3. Mr Promise Jacob – karamar hukumar Ahoada ta yamma

4. Dr Tamunotonye Peters – karamar hukumar Akuku Toru

5. Surveyor Atajit Francis –karamar hukumar Andoni

6. Barrister Ibiapuve Charles – karamar hukumar Asari Toru

7. Mr Kingsley N. Banigo – Karamar Bonny

8. Dr Sokari Ibifuro Francis – karamar hukumar Degema

9. Dr Gloria Obo Dibiah – karamar hukumar Eleme

10. Barr Franklin P. Ajinwon – karamar hukumar Emohua

11. Dr Onyemachi S. Nwankwor – ƙaramar hukumar Etche

12. Prof. Gospel G. Kpee – Karamar hukumar Gokana

13. Mr Isaiah Christian Nobuawu – karamar hukumar Ikwerre

14. Dr Barinedum Nwibere – karamar hukumar Khana

15. Dr Clifford Ndu Walter – karamar hukumar Obio Akpor

16. Dr Chukwuma Aje – kananan hukumomin Ogba/Egbema/Ndoni

17. Eliel Owubokiri – ƙananan hukumomin Ogu/Bolo

18. Mr Thompson Isodiki – karamar hukumar Okrika

19. Manager Ikechi Wala – karamar hukumar Omuma

20. Mr Fred Apiafi – kananan hukumomin Opobo /Nkoro

21. Eletuuo Ihianacho – karamar hukumar Oyigbo

22. Dr Sam Kalagbor – karamar hukumar Port Harcourt

23. Mr Nuka O. S. Gbipah – ƙaramar hukumar Tai

Sai kuma wadanda ya nada a matsayin shugabanni da mambobin hukumar zaben jihar da suka haɗar da:

1. Dr Micheal Ekpai Odey – shugaba

2. Mr Lezaasi Lenee Torbira – Mamba

3. Prof Author Nwafor – Mamba

4. Prof Godfrey Woke Mbgudiogha – Mamba

5. Prof Joyce Akaninwor – Mamba

6. Dr Olive A. Bruce – Mamba

7. .Prof Chidi Halliday – Mamba

Hakan ya biyo bayan hukuncin da kotun koli ta yanke, wanda ta bayyana zaben ƙananan hukumomin da aka gudanar a jihar a ranar 5 ga Oktoba, 2024, a matsayin mara inganci.

Matakin na zuwa ne sa’o’i kadan bayan wata babbar kotun tarayya da ke Fatakwal ta shirya ranar 14 ga Afrilu, 2025, don sauraren karar da lauyan kare hakkin dan Adam, Courage Nsirimovu na cibiyar Pilex Center for Civic Education Initiative ya shigar.

Nsirimovu na neman dakatar da nadin shugabannin kananan hukumomi a jihar.

Mai shari’a Adamu Mohammed wanda ke jagorantar al’amarin bai bayar da umarnin hanawa karara ba, sai dai ya umurci da a sanar da Shugaban rikon Jihar Rivers da ya bayyana dalilin da ya sa ba a amince da bukatar dakatar da nadin ba.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here