ADC a Jihar Kebbi ta tabbatar da tsohon Ministan Shari’a na Tarayya, Abubakar Malami, a matsayin dan takararta na gwamna a zaben 2027.
Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Mohammed Bello Doka, Mataimaki na Musamman kan Yada Labarai ga Malami, ya fitar, inda ya ce “shugabannin jam’iyya, masu ruwa da tsaki, da magoya baya sun nuna amincewa da shirin ADC na fuskantar zabe mai zuwa.”
A cewar sanarwar, tsohon hafsan soji, Aminu Bande, an tabbatar da shi a matsayin dan takarar majalisar dattawa na jam’iyya a Kebbi ta Tsakiya, yayin da tsohon Mataimakin Kwamanda Janar, Ibrahim Muhammad Mera, ya zama dan takara a Kebbi ta Arewa.
Ta kara da cewa Garba Danjuma Limi an tabbatar da shi a matsayin dan takarar majalisar dattawa na jam’iyya a Kebbi ta Kudu.
Sanarwar ta bayyana cewa jam’iyyar na ci gaba da himmatuwa wajen samar da shugabanci mai ma’ana, mulki nagari, adalci, tsaro, da ci gaba mai dorewa ga Jihar Kebbi da kasa baki daya.
Haka kuma ta yi kira ga ‘yan jam’iyyar da su hadi kai da kuduri tsakanin mambobi da magoya bayan jam’iyya, inda bayyana fatan cewa ADC za ta gina “makoma mai kyau ga tsararraki masu zuwa.”












































