Ƴan bindiga sun kashe wata mata tare da yi awon-gaba da wata mai yi waƙasa hidima, da kuma wasu mutunen a unguwar Kubwa da ke Abuja, babban birnin tarayyar Najeriya.
Lamarin ya faru ne a ranar Talata sa’ilin da ƴan bindigan suka kai hari tare da kwashe matasan takwas.
Bayanai sun ƙara da cewa mutane da dama sun tarwatse a lokacin da aka kai harin.
Wani shaida ya faɗa wa jaridar Punch cewa da farko mutum goma ne ƴan bindigan suka kwasa, sai dai biyu daga cikinsu sun tsere a lokacin da ake tafiya da su cikin daji.
Ya ƙara da cewa ƴan bindigan sun rinƙa yin harbi a daidai lokacin da suka isa domin tsorata mazauna yankin.













































