Ƴan bindiga sun sace mai yi wa ƙasa hidima a Abuja

FB IMG 16704119712077297
FB IMG 16704119712077297

Ƴan bindiga sun kashe wata mata tare da yi awon-gaba da wata mai yi waƙasa hidima, da kuma wasu mutunen a unguwar Kubwa da ke Abuja, babban birnin tarayyar Najeriya.

Lamarin ya faru ne a ranar Talata sa’ilin da ƴan bindigan suka kai hari tare da kwashe matasan takwas.

Bayanai sun ƙara da cewa mutane da dama sun tarwatse a lokacin da aka kai harin.

Wani shaida ya faɗa wa jaridar Punch cewa da farko mutum goma ne ƴan bindigan suka kwasa, sai dai biyu daga cikinsu sun tsere a lokacin da ake tafiya da su cikin daji.

Ya ƙara da cewa ƴan bindigan sun rinƙa yin harbi a daidai lokacin da suka isa domin tsorata mazauna yankin.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here